Monday, April 25, 2011

RAYUWAR BAHAUSHE A SABON KARNI

RAYUWAR BAHAUSHE A SABON KARNI
Duk lokacin da aka yi batun arewacin Najeriya, babu abin da zai fara fadowa mutum a rai sai Malam Bahaushe, domin harshen Hausa shi ne ya mamaye wannan yanki mai albarkar noma da mutane wadanda suka shahara ta fannoni daban daban, kama daga fannin ilmi, siyasa da kasuwanci, ga kuma fadin kasa ga Allah Ya ya wadatamu da ita. Kuma tarihi ya tabbatar cewa Bahaushe mutum ne mai karamci da haba – haba da sauran kabilu, musamman makwabtansa. Wannan ce ma ta sa harshen Hausa ya ya shahara ya rinka yaduwa a tsakanin wadannan kabilu.
Bahaushe mutum ne mai wayayyen kai, tun daruruwan shekaru da suka shude. Wannan ce ma ta sa ya yi fice ta fannoni da dama, ba ma a nahiyar Afirka ba , har ma a duniya baki daya. Wannan daukaka da Bahaushe ya yi ta jawo masa kwarjini a cikin gida da kuma waje. Wanda har ma a wadancan lokuta ake ganin Bahaushe da matukkar daraja, ta inda duk inda ya je ake ba shi kulawa ta musamman kuma yake ba wa sauran kabilu sha’awa.
Wani abin sha’awa Bahaushe bai bata lokaci ba wajen karbar addinin musulunci a matsayin fanninsa na rayuwa. Hakan ya kara masa daukakar da bata misaltuwa, wanda sakamakon haka ne aka haifar da shahararrun malamai da masana a wannan sashi na arewacin Najeriya.
Idan kuma muka kalli Bahushe ta fuskar siyasa za mu ga cewa, siyasar wancan lokaci ba ta cika ba tare da dan arewa ba. Domin shi ne wanda ya san dabaru da kuma luggar mulki da siyasa. Wannan ce ma tasa har aka samu mashahuran ‘yan siyasa a wannan sashi, wanda suka yi fice ta fuskar kare mutunci da kuma darajar wannan sashi da al’ummarta da kuma hadin kan kasa baki daya. Irin wadannan mutane sun hada da; marigayi Malam Sa’adu zungur, Sa Abubakar Tafawa Balewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna, da kuma irin su Malam Aminu Kano da dai sauransu.
domin al’umma shaida ne a kan irin tubalin siyasar da wadannan shahararrun ‘yan kishin kasa suka assasa musamman a wannan yanki na arewacin Najeriya, babu shakka sun yi kokari, ba karami ba. Hakan ce ta ba su damar shahara da kuma samun kwarjini a idanun duniya. Da akwai wani lokaci da Azikwuwe (Zik) ya hadu da Sardaunan Sokoto sai yake cewa da Sardauna “ya kamata mu manta da bambance – bambancen da suke tsakaninmu” amma Sardauna da yake Allah Ya yi masa hikimar iya magana da kuma zama da jama’a sai ya amsa masa da cewa; “ya kamata dai mufahimci bambance – bambancen da suke tsakaninmu, ni musulmi ne dan arewa, kai kuma kirista ne mazaunin kudancin kasar nan, fahimtar hakan ne zai sa mu samara da dunkulalliyar al’umma(kasa) mai dorewa”
To, amma idan muka kalli rayuwar Malam Bahaushe a wannan karnin da muke ciki, shin abin haka yake, ko kuma labari ya sha bamban? Matukar za mu yi wa kanmu hukunci na adalci za mu tabbatar cewa hakika labari ya sha bamban, ta fuskar siyasa, addini da kuma rayuwa ta yau-da-kullum. Dan uwa! Za ka yarda da ni idan na ce maka a yau rayuwar Malam Bahaushe tana cikin tsaka mai wuya. Domin a fadin duniya babu kabilar da ta mayar da bara hanyar cin abinci (ma’ana sana’a) sai Malam Bahaushe. Domin za ka ga yara, matasa da magidanta majiya karfi suna yawo kwararo – kwararo da garuruwa har ma da kasashen ketare, suna bara wai da sunan neman abinci. Alhali kuma akwai kasashe da kabilu da suka fi mu talauci, amma ba za ka same su da irin wannan dabi’a ba. Mu mutuwar zuciya ta hana mu mu nemi na kanmu.
Wani babban abin haushi kuma shi ne yadda ‘yan siyasa suke yin amfani da matasa, a matsayin ‘yan bangar siyasa. Abin takaici ma a nan shi ne yadda wadannan ‘yan siyasa suke saya wa matasa makamai da kwayoyi da sauran abubuwan sa maye wai domin su taimaka musu wajen tsoratar da abokan hamayya. A wasu lokutan ma har kashe junansu suke yi, wai da sunan yakin neman zabe. Ba ma a nan abin zai ba ka haushi ba sai ka ga yadda wadannan ‘yan siyasa suke daukar nauyin ‘yan daudu da karuwai suke sheke ayarsu, a duk lokacin da aka ce sun fita kanfen. wannan shi kansa abin takaici ne domin yakan haifar da koma baya da kuma rashin ganin wannan al’umma da mutunci.
Hakika marigayi Malam Sa’adu Zungur ya yi gaskiya, a wakarsa ta “Arewa Jamhuriya ko Mulukiya “ a inda yake cewa:
“Domin fa arewa da hargitsi,
da yawan barna ba kariya.

Matukar arewa da karuwai,
Walla za mu yi kunyar duniya.

Matukar ‘yan iska na gari,
Dan daudu da shi da magajiya.

Da samari masu ruwan kudi,
Ga maroka can a gidan giya”.

Sannan kuma Malam Sa’adu Zungur ya kara da cewa:
“Matukar yaranmu suna bara,
Allah ba ku mu samu abin miya.

A gidan birni da na kauyuka,
Da cikin makarantun tsangaya.

Sun yafu da fatar bunsuru,
Babu shakka sai mun sha wuya.

Shawarata a nan ita ce: lokaci ya yi da shugabanninmu na arewa za su farka dangane da kalubalen da yake fuskantarmu, ya kamata musamman gwamnatocin Jahohi da na tarayya da ma na kananan hukumomi da ‘yan majalisunmu, kai har ma da ‘yan boko da attajirai da malaman addini, su yunkuro wajen bayar da tallafi da kyautata tarbiyya a tsakanin al’ummar arewacin Najeriya, domin samar da al’umma ta gari.
Sannan kuma wani nauyi da yake wuyan ‘yan siyasa shi ne, ya kamata su rinka la’akari da halin da al’ummarmu take ciki na tabarbarewar al’amura, domin su rinka aiwatar da kyawawan manufofi da kudurori domin ganin an kyautata al’amura a wannan sashi.
Sai kuma wani nauyi da yake kan attajirai da kuma ‘yan boko; su kuma ya kamata su rinka kokarin ba wa matasa tallafi na jari da kuma na karo karatu, domin ganin an yi maganin zaman banza da shaye – shayen miyagun kwayoyi a cikin wannan al’umma.
Su kuwa matasa babban nauyin da yake kansu, shi ne su daina raina kananan sana’o’I, kuma su rinka kokarin dogaro da kuma neman na kansu, domin gujewa tozarta da zaman kashe wando.
A karshe ina kira ga al’umma baki daya, da mu hada kawunanmu domin ganin mun samar da al’umma ta gari, wadda za mu rinka alfahari da ita a duk inda muka tsinci kanmu. Domin hadin kai shi ne tushen ci gaban al’umma.
Malam Abubakar Ladan Zariya, yana cewa a wakarsa ta “Hadin kan Afirka”
“kwalama hadama ba zai bar mu,
ba mu kai ga mu cimma burinmu,
Son kai haka za girman kanmu,
Shi ke cutar mu da ‘ya’yanmu,
Ba ma kishi na magabatanmu.

Hakika magabatanmu sun yi kokari wajen ganin cewa ba su kawo rarrabuwar kai a cikin al’umma ba. Don haka ya rage namu mu zabi abin yi. Sa’adu Zungur yana cewa:
“mu dai hakkimu gaya muku,
ko ku karba ko ku yi dariya.

Dariyarku ta zam kuka gaba,
Da nadamarmai kin gaskiya.

Daga: Hamisu Musa Isah,

Shekar – Barde,

Kano state.

08068979409.

hamisu_isah­@yahoo.com

http:\\bahaushensabonkarni.blogspot.com

Sunday, January 11, 2009



AL’ADUNMU MUTUNCINMU: KOWA YA BAR GIDA, GIDA YA BAR SHI

Hamisu Musa Isah,

Shekar - Barde, Layin Gidan Maikantu,

Kumbotso L.G. Kano State

08068979409/08027996814

hamisu_isah@yahoo.com

Kalmar al’ada asalinta daga kalmar Larabci take. Kasancewar Bahaushe a ma fi yawan lokaci hankaka ne maiyar da dan wani naka. Sai ya ari kalmar yake yin amfani da ita. Kalmar al;ada dai a Hausance tana nufin hanyar gudanar da rayuwar al’umma. Musamman hanyoyin rayuwa na yau da kullum wadanda al’umma ta saba da su.

Kuma kowacce al’umma tana da nata al’adun wadanda take tunkaho da su. Muhimmin abin da ya kamata mu sani, kafin bayani ya yi nisa, shi ne, al’ada gida biyu ta rabu. Wani zai yi mamaki ya ji an ce al’adu sun rabu gida biyu. To, ba abin mamaki ba ne. Ta farko ita ce al’adun gargajiya, wadanda Hausawa suka gada tun iyaye da kakanni, kamar irinsu tufafi da tsarin sarauta da sauransu.

Game da kashi na biyu kuwa su ne, al’adu na aro, ma’ana bakin al’adu. Wadannan bakin al’adu su ne irin wadanda al’ummar Hausawa suka aro daga wasu al’ummomi, musamman wadanda suka yi ko suke yin cudanya da su. Wadannan al’ummomi za su iya zama makwabtansu na kusa da kuma na nesa.

Kafin na yi nisa bari na dan koma baya kadan. A nan zan dan yi wani tambihi ne game da al’adun Bahaushe na gargajiya. Domin mutane su fahimta cewa, akwai kyakkyawa, akwai kuma maras kyau. Kasancewar Bahaushe ya karbi addinin musulunci. Kuma ka’ida ce ta addinin musulunci yakan yi wa al’adun al’ummomin da ya samu abubuwa guda uku.

Na farko dai, idan wadannan al’adu sun dace da dokoki da kuma koyarwar addinin to yakan karba tare da bayar da kwarin gwiwar aiwatar da su. Abu na biyu kuma da addinin yake yi wa al’adu shi ne, yi musu kwaskwarima ko gyare – gyare domin su dace da dokoki da kuma koyarwar addinin. Abu na uku kuwa shi ne, addini yakan yi fatali tare da watsi da al’adu wadanda suka yi hannun riga da wannan addinin.

Kamar yadda muka fada a sama al’ada na nufin, hanyar gudanar da rayuwar al’umma. Wannan ce ma ta sa idan mutum yana son ya gane ko kuma ya fahimci al’adun wata al’umma, mataki na farko da zai bi shi ne, ya yi nazarin hanyoyin rayuwar wannan al’umma. Wannan ce za ta ba shi damar gane al’adun wannan al’umma.

Kamar kowacce al’umma, ita ma al’ummar Hausawa tana da nata al’adun wadanda suke yi mata jagoranci a hanyar gudanar da rayuwar al’ummarta. Sai dai ba a nan gizo yake saka ba. Wadannan al’adu sun gamu ko suna gamuwa da cikas ko kuma koma baya, musamman a halin da muke ciki a yanzu. Duk da cewar Bahaushe yana da himma da kuma kokarin kare martabar al’adunsa. To, amma mene ne yake jawo irin wannan koma bayan da ake samu, musamman ma a wannan lokacin da muke ciki? Akwai dalilai da yawa wadanda za a iya ta’allakasu da wannan halin da muke ciki. Daga cikin wadannan dalilai akwai na nesa da kuma na kusa. Daga cikin na nesa; za mu iya cewa dalilin ya samo asali ne tun lokacin da Turawan mulki mallaka suka shigo wannan yanki namu mai albarka na arewacin Nijeriya. Ma’ana lokacin da suka yi mana cin mutunci na farko, wato lokacin da suka samu nasarar far wa rundunar Sarkin musulmi Attahiru suka yi musu kisan kare dangi. Bayan sun yi musu haka ne suka dawo suka tambayi tsirarun sarakuna da suka rage, cewa ko da wanda yake son yin shahada irin ta Sarkin Musulmi Attahiru? A lokacin wasu daga sarakunan suka bi dare suka sulale, wasu tsiraru kuma suka mika wuya. To, in gajarce muku labari tun daga wannan mika wuya ne aka fara samun canji a al’adun Hausawa musamman ta fuskar mulki. Idan mai karatu bai fahimta ba bari na yi masa dalla – dalla ko zai fahimci abin da nake nufi na canjin da aka samu.

Wato dai daga wancan lokacin sai nadin sarki ya bar hannun Daular Usmaniyya dake Sokoto, domin kafin zuwan Turawa, Daular Usman dan Fodiyo ce take da iko da kuma alhakin nada sarki da ke karkashin wannan Daular. To amma zuwan Turawa sai suka ce daga wancan lokaci wannan ta kau. Ma’ana kowanne sarki cin gashin kansa yake yi. Turawa suka yi amfani da wannan dama da suka samu ne domin su rarraba kawunan sarakunan Daular Usmaniyya. Wato idan muka yi la’akari kuma muka yi nazarin wannan mataki za mu ga cewa al’adunmu na kwarai da suka fara raunana, su ne na zumunci da girmamawa da ke tsakanin wannan daula mai albarka ta Usmaniyya. Hakika wannan rauni da suka yi mana idan ba wani iko na ubangiji ba, har mu koma ga mahaliccinmu ba za mu iya magance shi ba. Hasali ma abin kullum dada lalacewa yake yi. Turawa sun yi mana haka ne, domin sun riga sun san inda baki ya karkata nan yawu ke zuba. Ma’ana sun fahimci cewa talakawa suna yin biyayya ne da kuma koyi ga magabata musamman sarakuna, don haka ne ma suka fara ta kan sarakunan. Da suka fahimci wasu daga cikin sarakunan sun mika wuya. Sai suka fito da wata sabuwar manakisar. Wato tsarin nan na mulki ta bayan fage “Indirect Rule” wanda shi kansa ya taka muhimmiyar rawa wajen gurbatawa da kuma nakasta kyawawan al’adun al’ummar Hausawa misali, tun da Turawa suka gabatar da wannan tsari ne sai sarakunanmu suka bar karbar oda daga daular Usmaniyya, sai dai daga wurin sarauniyar Ingila ta hannun Turawan mulkin Mallaka. Na tabbatar ba za ku bi ni bashin rantsuwa ba, idan na ce maku wannan ce ta jawo talakawa suka fara yanke kauna ga shugabanninsu (sarakuna) na wancan lokacin, domin a da suna ganin babu ya su amma yanzu sai ga shi ba su da ikon ma su zauna a fada sai da yardar Turawa. Don haka wannan ta sa talakawa suka fara saka wa wasu daga cikin sarakunan wancan lokacin ayar tambaya, suna tunanin shin kuwa wadannan su ne shugabanninmu da muka sani ko dai wasu ne daban. Marigayi Malam Sa’adu Zungur a wakarsa ta ‘Arewa Jumhuriya ko Mulukiya’ yana cewa:

“Don akwai wasu ma a sarakuna,

Mun bar su da ayar tambaya.

Hakkin jama’a na kansu duk,

Surike igiyarsa da gaskiya.

Don haka irin wadannan tambayoyi sai suka rinka saka tantama da kuma yanke kauna a zukatan talakawa ga shugabanninsu. Daga nan kuma sai Turawa suka fara bijiro da wasu matakan yaudarar suna nunawa talakawa cewa, su ne kawai za su iya fitar da su daga wannan kangi da suke ciki. Wanda dama haka suka shirya (Turawan). Domin dama sun zo ne don su farraka tsakanin talakawa da kuma shugabanni (sarakuna) na asali, cikin hikima da kuma yaudara. Saboda su samu su shiga tsakani. Bahaushe ma yana cewa: “sai bango ya tsage kadangare yake samun wurin buya”. Don haka suka rasa wurin fakewa sai suka yi amfani da karfi da kuma yaudara suka tsaga bangon suka shiga. Bayan ma sun shiga sai suka fara yin kokarin rushe katangar domin kada a sami wani maginin ya yi tunanin gyara wurin da suka tsaga. Marigayi mai alfarma sarkin musulmi Attahiru kafin ya yi shahada ya rubuta waka da ya saka mata ‘Wakar Zuwan Annasara’ a inda a ciki yake cewa:

“Idan iko kakai kak ko ki tashi,

Ina iko yakai ikon Nasara.

Idan sun baka kyauta kada ka amsa,

Dafi na sunka ba ka guba Nasara.

Suna foro garemu mu bar zalama,

Mazalumta da kansu diyan Nasara.

Bakar fitina gare su da kau makida,

Ta bata dinin musulmi Annasara.”

Saboda haka mataki na farko da suka dauka na kawar da sarakuna daga fagen mulki shi ne, mataki ko kuma na ce shawarar da suka yanke a shekarar 1914, wato shekarar da suka yi wa wannan kasar auren dole. Watakila mai karatu zai yi mamaki ya ji an ce an yi wa wannan kasar auren dole. To ba wani abu ake nufi da auren dole ba, sai lokacin da Turawa suka hade sassan kasar nan wuri guda, wato suka hade kudanci da kuma arewacin kasar nan, karkashin walliccin wani hatsabibin Bature wai shi Lugga “Lugard”

Hakika wannan aure ya jawo matsaloli musamman ma mu a nan arewacin Nijeriya ta fuskar kyawawan al’adunmu. Domin an je an dauko mana wasu mutane da ba mu da wata alaka da su daidai da ta cin abinci, an ce wai ‘yan uwanmu ne. Ba ma a nan abin ya tsaya ba, wai har nuna mana ake yi wai duk daya muke da su bayan kowa ya riga ya san akwai bambance – bambance mai tarin yawa a tsakaninmu. Wannan ya yi matukar kawo mana koma baya ta fuskar gudanar da mulki da kuma aiwatar da rayuwarmu ta yau da kullum. Malam Mudi Sipikin yana cewa a wakarsa ta “Itaciyar Zumunta”

“Me za mu ce da zamanin nan namu,

Domin cikinsa a yanzu babu zumunta.

Ko yalla ya jama’a kuna lura kuwa,

Yau ga shi duk al’adarmu an juya ta.

Manyan abubba masu kyau da muke da su,

Tun zamanin DA yanzu an lalata.

Tun zamanin da NASARA sadda ya bayyana,

Sha’aninmu al’adunmu an rushe ta.

Kuma ga abubba wanda ba su da kyan gani,

Sun afku sun wuce ma adai lasafta.

Kuma wata wauta da Turawan suke yi ita ce; wai sai su rinka cewa mu mance da wadannan bambance – bambancen da suke tsakaninmu(maimakon mu fahimci bambance – bambancen da suke tsakaninmu) mu zamanto kasa daya al’umma daya kuma wai makoma daya. Hakan ba laifi ba ne, to amma abin da ya fara fado min a rai shi ne, ta yaya mutum zai manta da asalinsa da addininsa da kuma kyawawan al’adunsa na gargajiya da ya gada tun iyayen da kakanni. Domin wannan kira da suke yi na munce da bambancin da yake tsakaninmu; suna yin kira ne da mu manta da asalinmu da al’adunmu da kuma addininmu saboda su sami damar cusa mana nasu gurbatattun dabi’un da al’adun. Allah ya saka wa hamshakin dan siyasa alokacin magabatanmu da alheri, musamman a inda yake cewa: “ Nijeriya kasa daya ce amma kowa ya san gidan ubansa” wannan batu haka yake domin kuwa kowa kansa ya sani da kuma al’ummarsa. Bai kamata na wuce wannan turbar ban kawo misalin wata hira da wasu manyan ‘yan siyasarmu na dauri suka taba yi ba, wato tsakanin Gamji Sa Ahmadu Bello Sardauna da kuma Azikuwie (Zik), yadda hirar tasu ta kasance kuwa shi ne, a lokacin da Zik ya hadu da Sardauna sai yake cewa: “ya kamata mu manta da bambance – bambancen da suke tsakaninmu”. A nan ne fa sai Sardauna ya ba shi amsa kamar haka: “A’a ya kamata dai mu fahimci bambance –bambancen da ke tsakaninmu. Ni dan arewa ne kuma musulmi, haka kuma kai (Zik) dan kudancin kasar nan ne kuma mabiyin addinin Almasihu. Ta fahimtar wadannan bambance – bambance ne za mu iya samar da hadin kai a wannan kasa tamu ( Nijeriya)”. Irin wannan matsayi da su Sardauna suka dauka ya dada jawo musu kwarjini a idanun duniya, ba ma wai nan kasa Nijeriya ba, har ma ake yi musu kallon tamkar iyaye ne a siyasar Afirka. Abin tambaya a nan shi ne wai shin su Sardauna barin asalinsu ne ya sa suka shahara ko kuwa riko da kyawawan dabi’u ne da kuma koyi da magabata ya sa suka shahara? Amsar wannan tambaya a bayyane take, saboda magabatanmu sun hango irin illar da take a tattare da tsarin mulkin da Turawan mulkin mallaka suka gabatar mana a wancan lokacin, don haka ne ma suka ki yarda su saki jiki da wannan tsarin domin fahimtarsu ya yi hannun riga da kyakkyawan tsarin da muka gada tun kaka da kakanni. Saboda haka ne ma suka rinka yin kokarin gargajiyantar da irin wadannan tsare-tsare da kuma fahimtar da al’umma da kuma wayar musu da kai game da dukkan wani tsari da aka gabatar musu da shi, wanda ya sabawa al’ada da kuma addini.

Abin da nake so a fahimta a nan shi ne ba wai kowanne tarko ne da Turawa suka dana mana muka fada ba. Domin mun yi nasarar tsallake wasu daga cikin wadannan tarakuna; kamar yadda wasu daga cikin tarkunan nasu (Turawa) suka kama mu a wuya.

Haka dai Turawa suka ci gaba da zabarin al’adunmu na kwarai da kuma addininmu domin ganin sun cusa mana sababbi marasa inganci. Gabatar da ilmin boko ya yi matukar tasiri ga rayuwar al’ummar kasar Hausa; kasancewar tun farko muna da tsarin ilmin addinin da kuma nakaltar yadda za a rubuta a kuma karanta haruffan Larabci. Kodayake makarantun farko da aka fara kafawa a garuruwan Lokoja da Wusasa ta Zariya na ‘yan Mishan ne. Shi kansa wannan dalili ya jawo gagarumin tarnaki ga karbuwa da kuma fahimtar ilmin boko. To amma daga baya gwamnatin Turawan mulkin mallaka ta kakkafa nata makarantun wadanda kafin a kafa su an yi wata kididdiga ta makarantun allo wanda su Turawan suka gano muna da makarantun addini sama da dubu ashirin da biyar a sakamakon binciken da Turawan suka yi da kansu. Ganin haka ne ya sa Turawa suka tabbatar zai yi musu wuya su gabatar da makarantun boko kai tsaye. Don haka sai suka fara da koyar da karatu da rubutu da kuma lissafi shi ne a Turanci suke ce masa “Tripple R ( Reading , Writing & Arithemetics)”. Kasancewar a Arewacin Kasar nan addinin musulunci shi ne kan gaba a cikin zukatan al’ummar wannan yanki sai suka rinka hadawa da koyar da Larabci; amma sai koyar da Larabcin ya zama kamar sinadarine, domin dama an tsarma shi ne domin a jawo hankalin al’umma su karbi karatun boko. Ba wai ina son na nuna cewa karatun boko ba shi da muhimmanci ba ne ba, a’a abin da nake so a fahimta a nan shi ne; su Turawa sun gabatar mana da karatun boko ne tun a wancan lokacin domin kawai su sami saukin gudanar da harkokin mulki. Saboda kudin da suke kashewa a wancan lokacin na harkokin gudanarwa ya yi yawa kasancewarkasar ta yi masu girma. Don haka ya zamar musu dole su jawo ‘an kasa domin taya su harkokin gudanar da mulki, don haka idan mun lura za mu fahimta cewa tun farko ba wai sun gabatar da karatun boko ba ne domi ilmantar da al’ummar Najeriya ba, sai domin biyan bukatar kansu. Daga baya ne kuma da tafiya ta yi nisa suka rinka shigar da wasu darussan har abin dai ya kawo yanzu.

Duk da cewa Turawasun san musulunci shi ne addinin da ya mamaye arewacin nijeriya, to amma ba su yi la’akari da haka ba a lokacin da suka fara gabatar da karatun boko a arewacin Nijeriya duk da cewa sun tsarma harshen Larabci da na Hausa a cikin manhajar karatun; to amma ba a ba shi muhimmanci ba a kan sauran darussa na boko ba. Haka kuma a tsara tafiyar karatun ba su yi la’akari da cewa Asabar da Lahadi ba su ne ranakun hutu a arewacin Nijeriya ba. Mu a wancan lokacin Alhamis da Juma’a muka sani ranakun hutu. Kuma kasancewar su ne ranakun hutu, mafi akasarin al’ummar kasar Hausa sun fi amfani da ranar juma’a domin kai wa ‘yan uwansu ziyara. Musamman yara, ana tura su gidajen ‘yan uwansu domin su kai ziyarar sada zumunci sannan su gaishe su. To amma kasancewar karatun bokko ya gifta ta Alhamis da Juma’a sai aka fara samun rauni ta bangaren zumunci da kuma ziyartar ‘yan uwa, wanda abin kullum dada lalacewa yake an gagara a gyara. Hangen haka ne ma ya sa marigayi Mallam Sa’adu Zungur yake cewa a cikin shahararriyar wakarnan tasa ta “Arewa Jumhuriyya ko Mulukiya”

“A arewa zumunta ta mutu,

sai nashadi sai sharholiya.

Shi kuma Mallam Mudi Sipikin cewa yake yi:

“Jama’a ku gane kar fa tarin dukiya,

ko don talauci har ku manta zumunta.

Ni dai nasiha ce nake nuna muku,

In kun bi lalle za ku san hairinta.

Don Allah kar Ibilis ya dinga batar da ku,

Ban zabe kaina har ku ce na manta.

Wani kokarinmu na son kasa ta yi arziki,

Wallahi sai mun lura mun daidaita.

Mu kula da hakkin ‘yan uwa mu yi taimako,

Ko masu hanya ne bare matalauta.

Mu kula ziyarar ‘yan uwa bisa ko washe,

Kullum mu zam lura muna gyarata.

Wallahi in dai mun kula har mun rike,

Dukkan jidali Rabbi zai maganta.

Akwai wata illa da Turawa suka yi mana wadda mtane da yawa ba su fahimce ta ba. Wannan ba wata illa bace illa raba shugabanni da talakawa; ma’anan idan mai karatu ya lura zai ga lokacin da Turawan mulkin mallaka suna jagorantar wannan kasa duk gidajensu a wajen gari suka je suka gina su, haka kuma ma’aikatu da kuma ofisoshingwamnati duk sai aka tsame su daga cikin al’umma (talakawa). Sabanin yadda muka saba a gargajiyance inda za ka ga gidan sarki a tsakiyar gari kuma koyaushe a cikin ganawa da talakawansa yake. To amma gogayen naka (Turawa) sai suka canja al’amarin. Kuma har yanzu haka al’amarin yake duk inda za ka ga gidan gwamnati ko sakatariyar karamar hukuma, to za ka gansua can gefen gari kewaye da jami’an tsaro kamar wani gidan kurkuku.

Wannan ce ta sa talakawa suke da shakku a kan shuwagabanninsu ta inda za a rinka samun misayar zafafan kalamai tsakanin shugabanni da kuma talakawan da ake mulka. Wanda a karshe za ka ga talakawa suna jifan shugabanninsu wanda yin hakan bakon al’amari nea cikin al’adunmu na gargajiya da ma addininmu.

Wani zagon kasa kuma da Turawa suka yi mana ta fuskar addini ita ta fannin aiwatar da shari’a. Lokacin da Turawa suka zo sun same mu da tsarin shari’a na musulunci wanda ta samo asali daga Alkur’ani da Hadisan Annabi. To, amma da zuwan Turawasai suka ce wai akwai gyara a tsarin tafiyarda shari’ar islama da muke yi, ganin cewa zai yi musu matukar wahala su kawar da tsarin shari’ar musulunci kai tsaye, sai suka kasa laifuka da kuma kotuna zuwa nau’ika biyu, ma’ana laifi ko shari’ar da suka shafi manyan laifuka, sai kai su kotunan da Turawan suke jagoranta. Amma shari’un da suka shafi rabon gado da rikicin aure da makamantansu sai aka bar su a kutunan da suke kiran su da sunan kotunan gargajiya, wanda suke yanke hukunci ta yin la’akari da abinda suka kitra da kundin dokokin shari’a (Penal Code).don haka aka jingine Kur’ani da Hadisi aka maye gurbinsu da tsarin “Penal Code” domin yanke hukunci.

Wannan irin katsalandan da Turawa suka yi mana ta fuskar shari’a ya yi matukarmayar da hannun agogo baya. Kasancewar irin jahadi da kuma dauki ba dadi da Mujaddadi Shehu Usman Dan Fodiyo ya yi don ganin ya tabbatar da tsarin shari’a da kuma daular musulunci a arewacin Nijeriya. Kuma ya ci nasara alokacinda gabadayan arewacin Nijeriaya da makwabtansu suka zama karkashin daular Usmaniyya. Wannan ce ta sa shari’ar musulunci ta kafu da digadiganta. Amma zuwan zuwan Turawan mulkin mallaka sai da suka targada ta, ma’ana suka yi mata kafa daya ta hanyar shigo da bakin abubuwa ta bayan gida.

Kamar yadda masan suka zayyana tufafin Hausawa suna daya daga cikin tufafin da ake tunkaho da su musamman ma yaddasuke da nau’o’I da dama kamar su: Binjima da kaftani da jauha da bulla da aska takwas ga kuma irin su barage da dasauran riguna wadanda Hausawa ke sakawa wanda idan muka ce za mu lissafto su lokaci ba zai bar mu ba. Kuma wani abin ban sha’awa shi ne, kowanne jinsi da kuma rukuni na mutane yana da nasa nau’in na tufafi. Misali, tufafin mata daban take da na maza. Haka kumatufafin saraki yasha bamban da na talakawa, sannan kuma tufafin malamai ya sha da na attajirai. Haka kuma na dattawa sun shabamban da na matasa. Wannan ce ma tasada kaga Bahaushe a zamanin da kai tsaye za ka gane irinmatsayinsa dakuma rukunin da ya fito a cikin al’umma.

Duk da baiwar daAllah ya yi mana ta wadatattun tufafi masu kima da alfarma, mun yi watsi da su a yau, wato mun yi abin nan da muke cewa ‘sakin na hannu kamun na guje’ ko kuma na ce ‘Jifan gafiyar Baidu’. Ma’ana mu muna yin kokarin watsi da namu tufafin, muna aro na wasu , wadanda ba su dace da al’adunmu ba. Irin wannan dabi’a tamu ce ta sa mashahurin marubucin wakokin Hausar nan Mallam Abubakar Ladan Zariya yake nusar da mu a wata waka da ya rubuta yake cewa:

“Jama’a mu bar sha’awar ado marar kwarjini,

wanda babu tushe, babu asali ko daya.

Mu yo adon suturunmu wanda muke da su,

Duka mai tsiraici yai ji kunyar duniya”.

Abin lura a nan shi ne, irin tufafin da muke yin amfani da su a yau, sun sabawa tarbiyya da kuma al’adunmu na gargajiya, ba ma wannan ba hatta addini bai amince da wasu daga cikinsu ba. Hakan ce ma ta saka a kullum mutuncinmu da kuma kwarjininmu suke zubewa a idanun duniya. Kuma wani abin takaici ma shi ne, irin wadannan tufafi da muke arowa ba su kai namu tafafin kwarjini da kima da mutunci ba. Domin wasu tufafin ma za ka ga bambancinsu da tsirara kadan ne ko ma a ce ba su da bambanci. Mallam Abubakar Ladan Yana cewa a wakar da ya rubuta:

“Kaya na sawa ba a fin mu daban-daban,

da Afirka, Esha, kasar Nasara gabadaya.

Hikimar mutan da ne da sunka yi kokari,

Mu ko kasala ta kashe mana zuciya”.

Sunday, September 16, 2007

MU FAHIMCI SIYASAR MAGABATANMU
Hamisu Musa Isah
Sheka – Barde Kano State, Nigeria.
+2348068979409
hamisumu@gmail.com
muhamisu@yahoo.com

Tun da farkon fari kafin na yi nisa ya kamata na dan waiwaya baya, domin na yi wa ‘yan uwa tuni, akan ma’anar siyasa ta zahiri da kuma badini. Duk da yake mutane sun fi sanin ma’anar siyasa na badini, sanadiyyar irin halin da suka tsinci kansu a ciki. Wannan bay a rasa nasaba da irin mummunar fahimtar da mutanenmu suka yi wa siyasa a wannan lokacin.
Ba tare da yin dogon bayani ba kowa ya san kalmar siyasa aro ta aka yi daga harshen Larabci wato, “ASSIYASAT” amma idan muka dubi ma’anar da Larabawa suka bawa kalmar shi ne: Hanyar mulki ko kuma hanyar sarrafa tunanin mutane domin shugabantarsu. A takaice dai za mu iya cewa siyasa tana nufin hanyar shugabantar al’umma. Wannan shi ne ma’anar siyasa ta zahiri.
Amma idan muka dauki ma’anar siyasa a hausance kokuma n ace ta badini ma’ana ta yadda jama’a suke kallonta a yau. Za mug a cewa takan dauki ma’anar; rashin cika alkawari ko wayo day audara, wasu ma suna yio mata kallon, neman hanyar kodamar handamar dukiyar mutane da cin amana ta hanyar yaudararsu da wasu kyawawan abubuwa da suke burin samu. Shi ne ma a yanzu idan mutum y ace “kar ka yi min siyasa” yana nufin karka yi min wayo ko kar ka yaudare ni. Wannan it ace ma’anar siyasa ta badini.
Bari kuma mu dubi dabiar ‘yan siyasa na da da kuma na yanzu. Ba sai na yi dogon bayani game da magabatanmu a fagen siyasa ba, domin kusan kowa shaida ne a kan irin tubalin siyasar da suka assasa musamman a wannan yanki na arewacin Najeriya, babu shakka sun yi kokari, ba karami ba. Duk da cewa dan adam tara yake bai cika goma ba, ma’ana su ma suna da nasu kurakuran, amma sai dai alkairansu sun fi kurakuran su yawa. Hakan ce ta bas u dammar shahara da kuma samun kwarjini a idanun duniya. Da akwai wani lokaci da Azikwuwe (Zik) ya hadu da Sardauna sai yake cewa da Sardauna “ya kamata mu manta da bambance – bambancen da suke tsakaninmu” amma Sardauna da yake Allah ya yi masahikima da kuma iya zama da jama’a sai ya amsa masa da cewa; “ya kamata dai mufahimci bambance – bambancen da suke tsakaninmu, ni musulmi ne dan arewa, kai kuma kirista ne mazaunin kudancin kasar nan, fahimtar hakan ne zai sa mu samara da dunkulalliyar al’umma(kasa)”
Sai kuma wani abin ban sha’awa ga magabatanmu, shi ne, sub a wai suna yin siyasa ba ne domin arzurta kansu, ko tara wani abin duniya. Mutum zai iya tabbatar da haka, idan ya dubi tarihin wadannan bayin Allah, za ka gad a yawansu sun bar mulki ba su da ko motar hawa da akwai ma wadanda suka bar mulkin ba tare da sun mallaki gida nasu na kansu ba, hasali ma wasu har bashi ake binsu. Kuma hakan bai hana sucimma nasara a rayuwarsu ba. Domin zai yi wuya gari yaw aye rana ta fadi ba ka ji an ambato irin ayyukan alkairin da wadannan bayin allah suka yi ba. Shi yasa ma za ka ga na makala sunayensu a wasu muhimman tituna da kuma gine – ginen gwamnati.
Wani kuma abin ban sha’awa shi ne, wadannan mutane siyasarsu bat a a mutu ko a yi rai ba ce, sukan bar talakawa su zabi wanda suke ganin shi ne ma fi alkairi a gare su. Haka kuma siyasarsu suna yin tan e a bias manufa. Domin kuwa za ka ga kowacce jam’iyya tana da manufofin da ta sa a gaba . wadanda take da niyyar aiwatar das u a lokacin da tai nasarar karbar mulki, kuma samun mulkin ba za sa su canja daga wadannan manufofin ba. Misali jam’iyyar PRP ta Malam Aminu Kano, daga cikin manufofinta sun yiwa talakawa alkawarin cewa da zarar sun zabe su, za su soke musu haraji da jangali. Kuma abin day a faru ke nan a lokacin da jam’iyyar PRP ta kafa gwamnati a wancan lokacin a Jihar Kano. Kuma manufofinta na kwatowa talakawa ‘yanci bai canja ba, hakan ne ya sa talakawa suka rike jam’iyyar hannun bi- biyu. Domin sun ga babu alamun yaudara a tattare da jam’iyyar da shugabaninta. To haka ake so kowacce jam’iyya ta kasance.
Haka ma su kansu talakawa a wancan lokacin suna yin siyasa ce ta akida ba wai don su sami abin duniya ba. Domin da yawansu sun yi gudun hijira a sakamakon bambancin ra’ayin siyasa haka kuma da ywa sun yi asarar ayyukansu duk sabuda bambancin ra’ayin siyasa. Haka kuma abin yake idan lokacin zabe ya zo,sukan tsaya ne su ga sun zabi wanda suke ganin ya fi musu alkairi a gare su. Ba wai wanda zai dauko kudi ya ba su ba. Shi ya sa ko da mutum yayi amfani da kudi a wancan lokacin bai cika kai labari ba. Wanann ce ta sa kowa yake ganin mutuncin kowa tsakanin masu zabe da kuma wanda aka zaba. Hatta su ma jami’an zabe sukan yi kokarin su ga sun yi adalci a tsakanin jam’iyyun da suka tsaya takara.
Haka kuma a wancan lokaci jam’iyyun hamayya bas a yanke hulda da jam’iyya mai mulki, musamman idan aka zo hakar gudanar da gwamnati, domin sukan ajiye siyasar a gefe sub a wa gwamnati a kan abin da suka ga zai kawo ci gaban al’umma. Haka ma ita gwamnati ba za ta bijire wa wadannan shawarwarin ba matukar dai tag a suna da amfani kasancewar abokan hamayya ne suka bayar da su. To haka ya kamata ‘yan siyasarmu na yanzu su zama.
Saboda haka nasihata ga ‘yan siyasarmu na wannan zamanin ita ce, ya kamata su ji tsoron Allah a kan duk wani abu da za su yi, domin tsoron Allah shi ne zai yi wa mutum jagoranci ya rika aiwatar da ayyuka na alkairi. Kuma su tuna cewa duk abin da suke yi a nan duniya akwai ranar hisabi, ranar da za a titsiye mutum zai yi bayanin irin ayyukan da ya aikata a nan duniya.
Haka kuma wani abu da ya kamata ‘yan siyasarmu su yi la’akarida shi, shin e magabatanmu ba wai sun yi siyasa ta a mutu ko a yi rai ban e; sukan ba wa kowa damarsa ya zabi wanda ya ga ya kwanta masa a rai, sub a su yin murdiyar zabe. Don haka ya kamata a rinka sakar wa talakawa mara suna zabar wadanda suka ga sun dace das u mulke su.
Nasihata ta gaba ita ce ya kamata ‘yan siyasa su guje wa handama da babakere da kuma wawurar kudin talakawa, wanda ya kamata su yi wa talakawan aiki, domin wannan zalunci mai girma, wanda a karshe mutum zai kare da yin nadama tun ma a nan duniya; za a iya fahimtar haka idan aka kalli yadda takasance a kan wasu tsofaffin gwamnoni wanda wasu daga cikinsu har hawaye suka zubar a gaban kuliya. Kasancewar bas u taba tunanin haka za ta kasance a game da su ba musamman a lokacin da suka shagala da wawurardukiyar talakawansu.
Bahaushe yace idan anbi ta barawo to abita ma bi sawu, domin su kansu talakawa suna da nasu laifin. Domin a kullum ka leka gidan wani maimulkin za ka gan shi a cike fal da ‘yan maula, kuma kowa da irin karyar day a je da ita domin kawai ya biya bukatun kansa. To, ya kamata mu ma talakawa muguje wa wannan mummunar dabi’a.
Allah Ya sa dai mu gane.

Friday, June 15, 2007

BAHAUSHE A SABON KARNI
Duk lokacin da aka yi batun arewacin Najeriya, babu abin da zai fara fadowa mutum a rai sai Malam Bahaushe, domin shi ne ya mamaye wannan yanki mai albarkar noma da mutane da kuma fadin kasa. Kuma tarihi ya tabbatar cewa Bahaushe mutum ne mai karamci da haba – haba da sauran kabilu, musamman makwabtansa. Wannan ce ma ta sa harshen Hausa ya rinka yaduwa a tsakanin wadannan kabilu.
Kasancewa Bahaushe mutum ne mai wayayyen kai, tun daruruwan shekaru da suka shude. Wannan ce ma ta sa ya shahara, ba ma a nahiyar Afirka ba , har ma a duniya baki daya. Wannan daukaka da Bahaushe ya yi ta jawo masa kwarjini a cikin gida da kuma waje. Wanda har ma a wadancan lokuta ake ganin Bahaushe da matukkar daraja, ta inda duk inda ya je ake ba shi kulawa ta musamman kuma yake ba wa sauran kabilu sha’awa.
Wani abin sha’awa Bahaushe bai bata lokaci ba wajen karbar addinin musulunci a matsayin fanninsa na rayuwa. Hakan ya kara masa daukakar da bata misaltuwa, wanda sakamakon haka ne aka haifar da manyan malamai a wannan sashi na arewacin Najeriya.
Idan kuma muka kalli Bahushe ta fuskar siyasa za mu ga cewa, siyasar wancan lokaci ba ta cika ba tare da dan arewa ba. Domin shi ne wanda ya san dabaru da kuma luggar mulki da siyasa. Wannan ce ma tasa har aka samu mashahuran ‘yan siyasa a wannan sashi, wanda suka yi fice ta fuskar kare mutunci da kuma darajar wannan sashi da al’ummarta. Irin wadannan mutane sun hada da; marigayi Malam Sa’adu zungur, Sa Abubakar Tafawa Balewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna, da kuma irin su Malam Aminu Kano da dai sauransu.
To, amma idan muka kalli rayuwar Malam Bahaushe a wannan karnin da muke ciki, shin abin haka yake, ko kuma labari ya sha bamban? Hakika labari ya sha bamban, ta fuskar siyasa, addini da kuma rayuwa ta yau-da-kullum. Dan uwa! Za ka yarda da ni idan na ce maka a yau rayuwar Malam Bahaushe tana cikin tsaka mai wuya. Domin a fadin duniya babu kabilar da ta mayar da bara hanyar cin abinci (ma’ana sana’a) sai Malam Bahaushe. Domin za ka ga yara, matasa da magidanta suna yawo kwararo – kwararo, suna bara wai da sunan neman abinci. Alhali kuma akwai kasashe da kabilu da suka fi mu talauci, amma ba za ka same su da irin wannan dabi’a ba. Mu mutuwar zuciya ta hana mu mu nemi na kanmu.
Wani babban abin haushi kuma shi ne yadda ‘yan siyasa suke yin amfani da matasa, a matsayin ‘yan bangar siyasa. Abin takaici ma a nan shi ne yadda wadannan ‘yan siyasa suke saya wa matasa makamai wai domin su taimaka musu wajen tsoratar da abokan hamayya. A wasu lokutan ma har kashe junansu suke yi, wai da sunan yakin neman zabe. Ba ma a nan abin zai ba ka haushi ba sai ka ga yadda wadannan ‘yan siyasa suke daukar nauyin ‘yan daudu da karuwai suke sheke ayarsu, a duk lokacin da aka ce sun fita kanfen. wannan shi kansa abin takaici ne domin yakan haifar da koma baya da kuma rashin ganin wannan al’umma da mutunci.
Hakika marigayi Malam Sa’adu Zungur ya yi gaskiya, a wakarsa ta “Arewa Jamhuriya ko Mulukiya “ a inda yake cewa:
“Domin fa arewa da hargitsi,
da yawan barna ba kariya.

Matukar arewa da karuwai,
Walla za mu yi kunyar duniya.

Matukar ‘yan iska na gari,
Dan daudu da shi da magajiya.

Da samari masu ruwan kudi,
Ga maroka can a gidan giya”.

Sannan kuma Malam Sa’adu Zungur ya kara da cewa:
“Matukar yaranmu suna bara,
Allah ba ku mu samu abin miya.

A gidan birni da na kauyuka,
Da cikin makarantun tsangaya.

Sun yafu da fatar bunsuru,
Babu shakka sai mun sha wuya.

Shawarata a nan ita ce: lokaci ya yi da shugabanninmu na arewa za su farka dangane da kalubalen da yake fuskantarmu, ya kamata musamman gwamnatocin Jahohi da na tarayya da ma na kananan hukumomi da ‘yan majalisunmu, kai har ma da ‘yan boko da attajirai, su yunkuro wajen bayar da tallafi da kyautata tarbiyya a tsakanin al’ummar arewacin Najeriya, domin samar da al’umma ta gari.
Sannan kuma wani nauyi da yake wuyan ‘yan siyasa shi ne, ya kamata su rinka la’akari da halin da al’ummarmu take ciki na tabarbarewar al’amura, domin su rinka aiwatar da kyawawan manufofi da kudurori domin ganin an kyautata al’amura a wannan sashi.
Sai kuma wani nauyi da yake kan attajirai da kuma ‘yan boko; su kuma ya kamata su rinka kokarin ba wa matasa tallafi na jari da kuma na karo karatu, domin ganin an yi maganin zaman banza a cikin wannan al’umma.
Su kuwa matasa babban nauyin da yake kansu, shi ne su daina raina kananan sana’o’I, kuma su rinka kokarin dogaro da kuma neman na kansu, domin gujewa zaman kashe wando.
A karshe ina kira ga al’umma baki daya, da mu hada kawunanmu domin ganin mun samar da al’umma ta gari, wadda za mu rinka alfahari da ita a duk inda muka tsinci kanmu. Domin hadin kai shi ne tushen ci gaban al’umma.
Malam Abubakar Ladan Zariya, yana cewa a wakarsa ta “Hadin kan Afirka”
“kwalama hadama ba zai bar mu,
ba mu kai ga mu cimma burinmu,
Son kai haka za girman kanmu,
Shi ke cutar mu da ‘ya’yanmu,
Ba ma kishi na magabatanmu.

Hakika magabatanmu sun yi kokari wajen ganin cewa ba su kawo rarrabuwar kai a cikin al’umma ba. Don haka ya rage namu mu zabi abin yi. Sa’adu Zungur yana cewa:
“mu dai hakkimu gaya muku,
ko ku karba ko ku yidariya.

Dariyarku ta zam kuka gaba,
Da nadamarmai kin gaskiya.

Friday, May 18, 2007

Hikimata

HARSHEN HAUSA DA KALUBALEN DA YAKE FUSKANTA.
A nan cikin Nijeriya harshen Hausa shi ne na daya a duk kasar, wajen yawan mutanen da suke amfani da shi. za a iya cewa harshen Hausa ya zama tafkin tsakiyar gari idan mutum bai sha ba to wani nasa ya sha. Ana iya cewa kusan ba lungu da sako da ba a magana da harshen Hausa a wannan nahiya.
Harshen Hausa mashahurin harshe ne a duniyar nan tamu,domin shahararsa ta kai ya goga ko ma ya yi kafada - da - kafada da dukkakn manyan harsunan duniya, domin harshe ne da yake da yalwar kalmomi da za a iya sarrafa su da bayyana kowanne irin tunani da su. Shi ya sa ma wani mawaki wato Malam Abubakar Ladan Zariya yake cewa a wakarsa:
"Harshenmu harshe ne a dangin harsuna,
Da muke gadara ko'ina nan duniya,

Har ma yi zaurance da waka ma da shi,
Tamkar su Turanci, Arab baki daya.

Za mu yi rubutu mu yi karatu ma da shi,
Mu alamta littaffai, jaridu bai daya.

Me zai hana ba za mu tashi mu girmama,
Harshe na kakanninmu babu kamar shiya."

Kamar yadda wannan mawaki ya fada, ana iya amfani da harshen Hausa wajen rubuta littattafai da jaridu da mujallu da kuma amfani da shi a kafafen yada labarai na radiyo da talabijin kai har ma da na'ura mai kwakwalwa.
Kodayake yaduwa da bunkasar harshen Hausa ba ya rasa nasaba da irin kwarjini da harshen yake da shi da kuma shaharar da Hausawa suka yi a fagen kasuwanci da fatauci. Hausawa sukan kutsa kowanne lungu da sako na wannan nahiya ta Afirka kai da ma duniya baki daya domin kai haja ko neman aiki ko neman ilmin addini da kuma yada shi. Haka kuma baki sukan yo takakka daga garuruwansu domin kawo haja da kuma saye a kasar Hausa. Wadannan da ma wasu dalilai suka sa harshen Hausa ya bunkasa ya shahara kuma ya gagara a wancan lokacin.
Kwarjini da kuma muhimmancin harshen Hausa a kullum kara bayyanuwa yake yi, kodayake har yanzu babu wata kasar Afirka ta yamma wadda ta mai da wannan harshe ya zama harshen kasa, amma a kan matsayinsa na farko daga cikin manyan harsunan Afirka, mutanen duniya suna daukan cewa babban kuskure ne idan aka banzatar da wannan harshe. Saboda haka manyan kasashen duniya kamar su: Amurka da Rasha da kasar Sin da Ingila da kuma Jamus suka ba wannan harshe babban muhimmanci. Kamar yadda kowa ya sani, wadannan manyan kasashe tuni suka fara yada labarai da harshen Hausa. Bayan haka wadannan kasashe suna kashe kudade da yawa wajen nazari da koyar da wannan harshe. Domin kuwa wani abin alfahari da tunkaho shi ne ba wata jami’a da ta yi shuhura a duniya da ba a koyar da harshen Hausa a cikinta. Wannan ma babban abin alfahari ne ga masu Magana da wanna harshe na Hausa. Kuma wani Karin abin alfahari ga wannan harshe da kuma masu Magana da shi, shi ne a jikin kudin kasarmu Nijeriya babu harshen wata kabila da aka yarda a yi amfani da shi sai harshen Hausa, ma’ana inda aka rubuta adadin kudin da Hausar ajami.
A nan gida Nijeriya haka zalika masana suna bayar da tasu gudummuwar ta fuskar himmatuwa wajen bincike da kuma bunkasa harshen, musamman ta fuskar rubuta littattafai da mukalu da wakoki, muna da irin wadannan mutane dubbai a cikin kasar nan kuma suna yin iya kokarinsu don ganin wannan harshe ya fadada kuma martabarsa ta karu a fadin duniya. Da akwai cibiyoyi da kungiyoyi da hukumomi wadanda suke karkashin wasu jami’o’i da kuma al’ummomin gari da suke ta yin aiki ba dare ba rana don ganin ci gaban wannan harshe.
Duk da irin wannan daukaka da kuma bunkasa da kuma kwarjini da wannan harshe yake da shi , wasu rukuni na mutane da ma daidaiku ba su ma san ana yi ba ‘wai kunu a wani gida’. Domin babban kalubalen da wannan harshen yake fuskanta shi ne, na rashin bin ka’idoji da dokoki da kuma tanade – tanaden wannan harshe. Wannan matsala tana ci wa manazarta da masana da kuma masu kishin wannan harshe tuwo a kwarya, domin matsalar ta zama ruwan dare, a inda za ka ga kafafen yada labarai musamman jaridu, wanda wasu da yawansu ba sa mutuntawa da kuma bin ka’idoji da kuma dokokin rubuta wannan harshe. Wannan babban kalubale ne da wannan harshe yake fuskanta, har ma wasu suna ganin cewa harshen Hausa ba shi da ma wasu tsayayyun ka’idoji da kuma dokoki. Har shi ne ma marigayi Dr. Akilu Aliyu yake cewa, a wakarsa ta “Bahaushe Mai Ban Haushi”

“Kwazo ya kyautu da mu nuna kuzari,
Inganta harshen namu shi ne Hausa.

Ku mu bar kasala sai mu himmatu kun ji,
Zazzage dantse nuna kishin Hausa.”

Haka ma marubuta littattafai, za ka ga wasu ko in ce da yawa daga cikinsu ba sa dora rubutunsu a mizanin wannan harshe, ma’ana ba sa bin dokoki da kuma ka’idojin wannan harshe. Don haka ne ma marigayi Dr. Akilu Aliyu ya kara da cewa:

“wannan abin kunya ina tamka tai,
Harshen wajen kakanka kai ka kasa,

Ya zam abin a yi dariya a yi gwalo,
A gareka don ka fadi ba shan fansa.”

Don haka ya zama wajibi a garemu da kuma duk wani mai sha’awar harshen Hausa, da mu himmatu wajen sani da kuma bin dokoki da kuma ka'idojin rubuta harshen Hausa.
Wata matsalar kuma da take ci wa wannan harshe tuwo a kwarya ita ce ta masu kafa allunan tallace - tallace na manya da kananan kamfanoni da ma hukumomi na gwamnati da masu zaman kansu, a inda za ka ga suna rubuta tallansu da kuma sanarwa da harshen Hausa yadda suka ga dama, ba tare da yin la'akari da dokoki da ka'idojin harshen ba. Wata Hausar ma da ake yin amfani ita a irin wadannan allunan talla , ba ma ta karantuwa.
Hanyoyin magance wadannan matsalaloli su ne:
Ya kamata kafafen yada labarai musamman ma na jarida su danga daukar kwararru, wadanda suka san ka'idoji da kuma dokokin wannan harshe na Hausa, domin kauce wa irin kurakuran da muka ambata a sama.
Bayan haka kuma manyan makarantu da jami'o'inmu musamman sashen koyar da harshen Hausa na wadannan makarantu, su tashi tsaye wajen fadakar da al'umma da kuma ilmantar da su, ta hanyar rubuce -rubuce da kuma bin diddigin irin wadannan kukrakurai domin kawo gyara.
Sannan kuma yana da kyau idan cibiyoyin nazarin Hausa a wadannan jami'o'i su dinga shirya bita akai -akai ga ma'aikatan yada labarai ('yan jarida) da kuma marubuta da masu buga takardu da littattafai domin ganin an kawar da wannan matsala baki daya.
Sai kuma shawara ta karshe, ya kamata su ma kansu malamai da suke koyar da harshen Hausa a makarantun Firamare da Sakandare, su dinga samin damar zuwa karop karatu akai - akai, idan ma haka ba ta samu ba, to, ya kamata a dinga shirya musu bita su ma daga lokaci zuwa lokaci.
Wadannan nan matakai idan aka bi su za a rage irin hawan kawarar da ake yi wa harshen Hausa. A karshe nake rufewa da wakar Malam Sa'adu zungur inda yake cewa:
"mu dai hakkinmu gaya muku,
Ko ku karba ko ku yi dariya.

Dariyarku ta zam kuka gaba,
Da nadamar mai kin gaskiya."